Friday, October 14, 2022

Ana gab da fara yaƙin neman zaɓen Barau.


Ana gab dab da fara yaƙin neman zaɓen Barau.

✍️ Abdul gaffar isah

Kwamitocin yaƙin neman zaɓen sanata Barau Jibrin, na kafafan sada zumunta na gab da fara aiki.

Hakan dai na ƙunshe cikin wata sanarwa da babban kwamitin ya fitar wadda Ibrahim Abdullahi Muhammad ya wallafa.

Sanarwar tace "wannan kwamiti na matasa da ɗalibai na shirin ƙirƙirar wasu kwamitocin dan nemawa Sen. Barau I. Jibrin ƙuriu a Dukkan ƙananan Hukumomin da yake wakilta.

Ibrahim yace "kwamitocin zasu yi aiki tuƙuru ba dare ba rana dan cimma burin su, ya kuma ƙara da cewa zasu fitar da Hazikan mutane waɗanda zasu iya nemowa jam'iyyar APC nasara a dukkan kujeru.

Zuwa yanzu dai akwai kwamitoci guda 3 na ɗalibai da ƴan midiya da zasu iya fara aiki.

1.  Bys Shuwaki  Daraktan Kafar sadarwa ta Zamani (Social Media)

2. Isyaku Abubakar Balan Daraktan Matasa

3. Yahaya Usman Kabo  Daraktan Dalibai

No comments:

Post a Comment