Friday, October 14, 2022

Bayan shafe watanni takwas, kungiyar ASUU ta janye yajin aikin da take yi.

  B


ayan sha fe watanni takwas, ƙungiyar ASUU ta janye yajin aiki

✍️ Abdul gaffar isah

Kungiyar malaman jami’a a Najeriya, ASUU ta sanar da jinkirta yajin aikin da mambobinta suka shafe wata takwas suna yi.

Dokta Chris Piwuna, mataimakin shugaban kungiyar ta ASUU ya tabbatar wa gidan rediyon BBC labarin, inda ya ce an janye yajin aikin ne da sanyin safiyar yau Juma’a, bayan da shugabannin ƙungiyar suka gana cikin dare a Abuja babban birnin kasar.

Kotun kolin Najeriya ta umarci kungiyar ta janye yajin aikin gabanin ta saurari daukaka karar da ta yi a gabanta.

Tun ranar 14 ga watan Fabrairun wannan shekarar malaman jami’o’in gwamnatin tarayyar Najeriya suka tsunduma cikin yajin aiki, suna neman gwamnatin ta biya musu wasu bukatu.

No comments:

Post a Comment