Saturday, October 15, 2022

 Yan Najeriya sun samu dubbunan kudade.


✍️ Saifullahi Abdulhamid Shu'aibu


A jiya ne yan Najeriya da dama suka samu dubban kudade ta lalitar bankanansu.


Mun samu labarin irin dubbunan kudade da yan Najeriya suka samu ta lalitar bankunansu, sai dai bamu rahoton musbbabin abin da ya sa ake tura kudaden ba amma dai shaidu da dama sun tabbatar da samun wannan kudi.


Wani shaidar gani da ido ya tabbatar mana da cewa mafi akasari anfi turawa mutane naira dubu hurhudu kai wasu ma har dubu sha biyar.


Badamasi Aminu wanda aka fi sani da Bass Alkanawui daya ne daga cikin wakilan Muryar Dawakin Tofa ya shaida mana cewa shima yau ya samu sakon dubu hudu ta bankinsa kuma yana tsammanin irin wannan kudaden ne da ake turawa yan Najeriyar se dai ya shaida cewa yana tsammanin kudaden daga babban bankin kasa CBN a turance ake tura kudaden.


Zamu cigaba da bibiyar labarin domin kara gano wadanda suka samu nasu sakonnin.


No comments:

Post a Comment