Wednesday, November 2, 2022

An bawa Abba Ganduje lambar yabo.

 A


n Karrama Engr Umar Ganduje a Matsayin Kwararran Injiniya Tare da Lambar Girmamawa ta FNSE.

Mai Girma Dan Takarar Majalisssar Tarayya Engr Umar Abdullahi Umar Ganduje , ya  Samu Lambar Girmamawa a Matsayin Cikakken Engineer Wato FNSE Wanda Kungiyar Injiniyoyi ta Kasa Wato (Nigerian Society of Engineers) ta Tabbatar Dashi Tare da Mika masa Lambar Girmamawa, A wani Biki da Suka Gudanar a Karo na 21a Dakin Taro na Hotel din Chida Dake Utako a Babban Birnin Tarayya Abuja.

Engr Ganduje, An Haife shi a Karamar Hukumar Dawakin Tofa Dake Jihar Kano, ya Kammala Karatun Digirinsa na Farko a Fannin Wutar Lantarki a Jami'ar Sharja Dake Daular Larabawa, Daga Bisa ya kara Samun Digiri na Biyu (Master's) Tare da Sakamako Mafi Daraja na Daya Wato Distinction a Fannin Sadarwa a Jami'ar Buckinghamshire Dake Kasar England,  Baya ga Samun Shedar Kammala Karatun Diploma a Fannin Sadarwa da wayoyin Hannu a Makarantar Commonwealth a Shekarar 2018.

Engr Ganduje, ya Shugabanci Gurabe Dabam Dabam Wanda Suka Danaganci Injiniyoyi Tare da Shiga Kungiyoyin Sadarwa, Engr Ganduje, ya Zama Babban Mataimaki Wato Senior Legislative Aide, a Offishin Mataimakin Shugaban Majalisssar Tarayya ta Kasa Wato Deputy Speaker Office.

Kafin Wannan, Engr Ganduje, Yayi aiki a Maaikatar Sadarwa ta NCC Tare da Rike Manager a Sashen USPF a Maaikatar Baki Daya, baya ga Haka Ya Samu kwarewar Aiki ta Shekaru Goma Tare da Harkar Gwagwarmaya a Fannoni Dabam Dabam.

Yanzu Haka Engr Ganduje, Shine Dan Takarar Majalisssar Tarayya Wanda zai Wakilci Kananan Hukumomin Dawakin Tofa Rimingado da Tofa Daga Jihar Kano a Jamiyar Apc da Yaddar Allah.

Taron ya Samu Halattar Mai Dakin Gwamnan Kano Prof Hafsat Abdullahi Ganduje,  Direktocinsa Karkashin Direkta General Dr Junaidu Yakubu Muhd, Kwamishinoni, Dan Takarar Majalisssar Jiha Hon Salisu Musa Gulu, Shugabannin Kananan Hukumomin Dawakin Tofa da Tofa, Masu Bawa Gwamna Shawara a Fannoni Dabam Dabam. Yau
TALATA 1 November 2022.

No comments:

Post a Comment