Monday, November 7, 2022

Wani yaro ne yake tafiyar da Gwamnatin kasar nan ba Buhari ba. -- Aranfosu.

 

Shugaban ƙaramar hukumar Nasarawa Auwal lawan shuaibu Aranfosu yace "Ba shugaba Buhari ne yake tafiyar da harkokin ƙasar nan ba, wani yaro ne.


Hakan na ƙunshe ta cikin wani sharhi da ya wallafa a wani rubutu da Marzuk Ungogo ya wallafa a shafin sa na facebook.

Marzuk dai yayi magana ne kan tattaunawar da akayi da shugaba Buhari game da lamurran kasar nan, ya kuma nuna cewa Buhari be amsa tambayoyin da akayi masa dai-dai ba.

Jim kaɗan bayan wallafa rubutun ne Auwal Aranfosu ya rubuta nasa sharhin kamar haka: " Marzuq Ungogo Wani yaro ne fa yake tafiyar da Gwamnatin ba Baba Buhari ba sai dai muyi hakuri da abun da muka gani.

Rubutun nasa dai yaja cece kuce, se dai Aranfosu bai sake cewa komai ba.

No comments:

Post a Comment